Sunday, September 16, 2007

YAN'UWAN TAKA DA SHARUDDANTA


Allah madaukain sarki yana gaya mana acikin alqur,ani mai girma cewa 'innamal mu,uminina ikhwah' lalle muminai yan uwan juna ne dan haka yan uwantaka tare da kyakkyawan mu,amala ta wajaba ga musulmi dan mu,amala da kyawawan halaye suna daya daga abubuwan da yasanya da yawa suka shiga musulunci manzon Allah (s.a.w) ya koyar damu kyawawan halayensa dan mubi kuma Alla ya yabe shi cewa (Innaka la,ala khulqin azeem) lallai manzon Allah yana kan kyawawan dabi,u masu girma.
Manzon yayi haquri da mutane tare da mayar musu kykkyawa in har an masa mummuna to yana ramawa da kykkyawa babban misali abinda ya faru tsakaninsa da bayahude maqwabcinsa da yake sanya masa shara kullum aqofar gida amma bai taba masa magana ba, sai wata ran manzo ya fito gida bai ga shara ba ya tambaya ina mai zuba masa shara kullum aqofar akace ai bashi da lafiya sai fiyayyan halitta ya tafi ya duba shi bayan yaje yasameshi akan shinfidar mutuwa sai manzon Allah ya umarce shi da yayi kalmar shahada dan shiga musulunci sai ya karkata kai ya kalli babansa ,sai baban ya masa umarini da ya amsa kiran manzon Allah ,ya amsa yayi kalmar shahada ya musulunta kuma ya cika da imani.

kenan kyawawan halaye suna da kyau da jan yan uwamu a tafarki na gari.
Manzon Allah yana cewa (DAYANKU IMANINSA BAYA CIKA HAR SAI YASOWA KANSA ABINDA YASOWA DAN UWANSA)

SHARUDDAN YAN UWANTAKA;

  • Takasance domin Allah.
  • Takasance a musulunci.
  • Takasance an yita tare da imani da tsoron Allah.
  • Takasance angina ta dan yiwa juna nasiha domin Allah.

HANYOYIN BUNQASA YAN'UWANTAKA:

  • Idan mutum yaji yana son dan uwansa ya sanar dashi.
  • Idan ya rabu da dan uwansa to yaringa masa addu,a abayan idonsa.
  • Idan ya hadu da dan uwansa yayi gaggawar masa sallama tare da musafaha(miqa masa hannu).
  • Ya yawaita ziyarar dan uwansa lokaci-lokaci.
  • Taya shi murna aduk lokacin da abin farin ciki ya sameshi da yi masa jaje idan wani abin baqin ciki ya sameshi.
  • yi masa nasiha da wasiyya da haquri yayin rashi,ko masifa atare dashi, da yi masa ta,aziyya in an masa mutuwa.
  • Ya tai maka masa aduk lokacin da buqatar hakan ta taso.

Allah yasa mu dace yasanmu daga cikin masu tsira.

wassalamu alaikum

MARABA DA RAMADAN (2)

Yan,uwa .... Assalamu alaikum

Barkanku da sake haduwarmu a maraba da ramadan kashi na (2).

Ya inganta manzo (s.a.w) yana yiwa sahabbansa bushara da zuwan watan azumi, manzon Allah yace"Idan farkon daren azumi ya kasance ana bude qofofin aljanna gaba daya ba tare da an rufe ko qofa daya ba, kuma ana rufe qofofin wuta baki daya ba tare da an bude ko guda daya ba, kuma akatange shaidanu,sai mai kira yayi kira ina mai neman alheri ya kusanto, ina mai neman sharri ya qaranta, Allah yana da yan'tattu daga wuta akowane dare."

Azumi na da falalar gaske daga ciki akwai shu,urin cewa dukkan al,umma dayane suna cin abinci lokaci daya kuma suna kame baki alokaci daya, mai kudi zaiji ni,imar wadata sai ya taimaka ma talaka,kuma yana qara tsoron Allah.

ABUBUWAN DA SUKA KAMACI MAI AZUMI;

  • Yawaita biyayya ga Allah tare da gujewa abubuwan da aka haneshi yayi da kiyaye farillai, da nisantar abubuwan da aka haramta.
  • yin sallah akan lokaci da halartar jam,i ga namiji cikin sallolinsa biyar dan manzon Allah yayi umarni da yin sallah acikin jama,a har yake cewa naso ace na umarci wani yaja sallah ni kuma in bi wadanda basa halartar sallah da jama,a da qirare na wuta aqona su, dan haka zamuga sallah a jam,a akwai shi da muhimmanci tunda har manzon Allah ya fadi hakan.
  • Nisantar qarya da cin naman mutane (gulma) da algus da mu,amala da riba ga yan'kasuwa da duk wani aiki ko magana wanda yake haram ne.Manzon Allah yace" wanda bai bar fadin qarya da aiki da ita ba da jahilci, Allah baya buqatarsa da yabar ci da sha dan shi."
  • Nisantar almubazzaranci a wajen abinci fadin Allah madaukakin sarki( kuci kuma ku sha amma kada kuyi israfi(barna) dan Allah baya son masu israfi) in yayi yawa to abayar sadaka.
  • Yin sallar tarawih (asham) a maallaci tare da jama,a tare da tsoron Allah da kuma halarto zuciya ayayin yin sallah , yawaita nafilfilin dare da na rana.
  • Yawan karatun alqur,ani da neman sanin fassararsa, da yawaita addu,o,i, sadaka, agazawa mai rauni, ciyar da mai azumi abin buda baki, yazo ahadisin manzon Allah (s.a.w) "wanda ya ciyar da mai azumi abin buda baki yana da kwatankwacin ladan mai azumin ba tare da an rage ladan mai azumin ko kadan ba. kuma an gafarta masa zunubansa an yan"tashi daga wuta" Allah yana bada ladan ga wanda ya baiwa mai azumin abinda zai buda baki ko da madara,ruwan sha, dabino. duk wanda ya shayar da mai azumi Allah zai shayar dashi daga qoramar manzon Allah.
  • umarni da kyakkyawa da hani da mummuna, kiyaye kai daga abubuwan da basu da amfani.
  • Fidda zakka ga mutumin data wajaba akansa in har lokacin fitarwa yayi kafin azumi ko bayan azumi,amma in yasaba ma kansa fidda zakka din a azumi yana da kyau saboda samun miskinai da masu rauni da kuma ninkuwar ladan ayyuka a wannan wata mai alfarma.

Yan"uwana musulmi Allah yasa mu dace ya kuma sanya muna cikin yan tattu daga wuta.

ameen

wassalamu alaikum warahmatullahi ta,ala wabarakatuhu.

Friday, September 14, 2007

Masjid As-Sanhuri - Sudan

عن أبي هريرة رض الله عنه أن رسول الله صلى الله عليه وسلم قال
من قام رمضان إيمانا واحتسابا غفر له ما تقدم من ذنبه- متفق عليه


My Master's Dissertation

Monday, September 10, 2007

DAGA MANYAN ZUNUBAI

Manzon Allah (s.a.w) yace:( daga manyan zunubai mtum ya la,anci babansa!)
sai sahabbai suka tambayi manzon allah ta yaya mutum zai la,anci babansa????!
manzon allah yace: idan mutum ya zagi baban wani to kamar ya zagi babansa ne, idan yazagi mahaifiyar wani kamar ya zagi mahaifiyarsa ne. ( bukhari da muslim)

kada mutum yai hakan ko da wasa!.

MARABA DA MAI ALBARKA

Godiya ta tabbata ga ubangijin da ya sanya ramadan watane na kankare zunubai da qara lada da daga darajojin dan adam , ramadan watane farkonsa rahma,tsakiyarsa gafara ,qarshensa yan' tarwa daga wuta.
abubuwan da yakamata mai azumi ya gudanar dasu yayin zuwa wannan wata mai albarka ;

1) TSORON ALLAH ; duk lokacin da ka kiyaye biyayya ga allah kuma zuciyarka ta cika da tsoron allah tare da ganin girmansa da tsoronsa, domin shi tsoronsa shine zuciyarka taji tana binsa kuma tana hanuwa da dukkan abinda ya hana.
tsoron allah yakansa mutum yayi abu tsakaninsa da mahaliccinsa kamar yadda yazo acikin tarihin zainul abidyn (ya kasance tsawon shekara 10 yana ciyar da mutane babu wanda ya sani har sai da ya mutu anzo masa wanka aka ga abayansa akwai alamar dan dako gashi, shi ba dan dako ba sai akaji kuma gidajen talakawa a madina suna kukan basu da abinci alhali sun kasance in suna tashi da asuba suna karo da buhun abinci aqofar gida ba tare da sun san wa ya aje ba sai da zainul abdyn ya mutu suka ga abinci ya dauke suka san wa ka aje musu, yayi hakane dan ya kasance aikinsa tsakaninsa da allah ne kawai ba tare da wani dan adam ya sani ba). dan haka ake son mutum ya kasance yana da aiki da yake ba wanda ya sani daga shi sai mahaliccinsa kamar yadda sahabbai da dama sunyi hakan hasanul basari yake cewa ( mun riski wasu daga sahabbai dayansu yakan kasance tare da iyalinsa ashinfida amma idonsa na zubar da hawaye na tsoron allah ba tare da iyalinsa sun san me ke faruwa ba) kuma sukan hadu daya ya zubda hawayensa don tsoron allah amma yana boyewa kar dan uwansa ya san me yakeyi allah yasa mu dace.

2) ADDU,A; koda yaushe dan neman tsoron allah ( allahumma inni a,uzu bika an ushrika bika shai,an a,alamuhu wa astagfiruka lima la a,alam.

3) TUBA; ka tuba ga allah ga dukkan zunubanka tuba na gaskiya fadin allah madaukakin sarki;( ku tuba zuwa ga allah baki dayanku yaku muminai ko kwa samu babban rabo.)

yan uwan musulmai ina muku murna da isowar wannan wata mai alfarma tare da yasamu cikin yan tattu daga wuta.

yar,uwarku
amatullah hajir ( um_ ja,afar)